ALAKAR KWARONA DA ZANGA-ZANGA

Shekarar 2020 ta shiga tarihi a matsayin wadda ta fi muni a tarihin da kimanin mutane kusan biliyan takwas da ke wannan duniya ba su taba ganin irinta ba. Ba tare da harba bindiga ko tura sojoji ba, akasarin mutanen duniya, walau masu mulki ko talakawa, matalauta da mawadata tamkar akuyoyi an tura mu cikin gidajenmu na zama tamkar a kurkuku tsawon watanni. Hakika na yi imanin cewa wannan annoba ta kwarona wata hanya ce da Allah ya nuna karfin ikonsa, ko mutanen duniya za su saduda su rage dagawa da girman kai da kuma wa’aztuwa. Amma da alamu duk darasin da cutar ta zo da shi ban ga alamun mun koye shi ba. A halin yanzu bazuwar annobar kwarona a karo na biyu na ci kamar wutar daji a kasashen turai da amurka, amma cikin ikon Allah ya kare mu yan Afirka, yadda yayin da kasashe a Turai ke kokarin sake kulle kawunansu a gidaje, mu muna ta harkokin mu tamkar babu ciwon. Idan ba Allah ba wa zai iya kare Afirka, nahiya mafi talauci da rashin tsari na shugabanci mai adalci, daga wannan masifa?

A nan Najeriya ko a karon farko na bazuwar wannan annoba ba ciwon ne ya fi yi mana illa ba irin yunwar da ta haddasa. Yayin da kasashe ke fitar da tallafi iri-iri domin tallafawa mafiya rauni a kasashensu ta hanyoyi daban daban, mu a nan Najeriya ba wanda ya kula da talaka. Gwamnati ta garkame mutane ba tare da wani kyaykyawan tsari ba amma kuma mawadatanmu sun rika mikawa gwamnati tallafin kudade maimakon su taimaki mutanensu da abubuwan masarufi. A Kano, biyu cikin mafiya arziki a jihar sun samar da cibiyoyin killace masu cutar kwarona maimakon su taimakawa talakawa da abinci. A tsakiyar kullen yayin da matasa a wasu sassa na birnin Kano su ka fara tare motocin abinci su na kwacewa, ni da kaina na yi wani sakon murya da aka turawa matar shugaban kasa Aisha Buhari wanda bayan ta saurara a kasa da sa’o’i 48 ta tura da kayan tallafin abinci na miliyoyin nairori birnin Kano, kuma ba ta mika shi ga gwamnati ba, sai ta saka mutanenta su ka raba ga talakawa kai tsaye. Amma tallafin da gwamnatin tarayya ta tura jihar Kano akwai wadanda aka bari a waje har ruwan sama ya lalata wasu sannan kuma wasu aka boye su a rumbunan ajiya.

Da langa, kuma a firgice talakawan kasar nan su ka fito daga cikin kullen kwarona saboda tsananin wahalar da su ka sha, amma cikin nutusuwa su ka koma kan ayyukansu domin neman abin sakawa a bakin salati. Katsam a wannan yanayi na kokarin murmurewa yayinda wasu ma sun rasa hanyoyin cin abincin su sai kuma gwamnati, a cikin sa’o’i 24 su ka sanar da karin kudin man fetur da wutar lantarki. Tun da aka kafa kasar nan ba’a taba ganin rashin tausayi da rashin imani da kuma nuna halin ko-in-kula daga mahukunta irin wannan ba. Mutane sun yi watanni cikin masifu da matsi ba tare da wani tallafi ba amma daga fitowa a sake matse su haka? Kuma a karshe zaka ga cewa duk abinda za’a tatsi talaka zai bige ne wajen ci gaba da kasha dawainiyar almubazzaranci mahukunta. A wannan gwamnati ne kasar nan ta karbi kofin zama kasa wadda ta fi kowacce kasa a doron duniya yawan matalauta (kimanin mutane miliyan 89 kafin annobar kwarona inda muka buge kasar India daga matsayin na daya). Yanzu Allah kadai ya san yawan mutanen da su ka karu cikin wancan jeri sakamakon yadda kwarona ta rusa ayyukan mutane da dama. Ana tsakiyar kwarona gwamnati ta sake duba kasafin kudi na 2020 inda, maimakon ta rage shi sakamakon kudaden shiga sun ragu, sai ta sake kara shi sama kuma mun san cewa a duk shekara akasarin kason wannan kasafi na tafiya ne ga mahukunta da ma’aikatan gwamnati inda kaso 40% ke zama kudaden gudanarwa na yau da kullum sannan kashi 25% ke tafiya wajen biyan basuka, sannan sauran kaso 35% din kansa ake yi kashe mu raba da mahukunta da yan ayyukan da a ka ware na raya kasa. Wannan dalili ya sa duk shekara ba’a ganin wani canji a rayuwar talaka bayan kasafin kudin domin ba wajensu ya ke tafiya ba.

Idan za mu gaya wa kanmu gaskiya, kowa ya san cewa ba wai fushin hukumar SARS ne kawai ya tunzura yan Najeriya wajen yin zanga-zanga ba illa dai azabar matse tattalin arzikin talakawa da hukumomi ke yi ce a gaba wajen wannan tunzuri. Koda yake dai akwai makiyan gwamnati wadanda su ka so yin amfani da zanga-zangar domin kawowa gwamnatin Buhari cikas. Amma daga gwamnatin har makiyan na ta basu fuskanci zanga-zangar yadda ya kamata ba, domin sun raina irin matsi da fushin da matasa ke da shi. Duk wanda ke hakilon juyin-juya-hali ta karfi tsiya a Nijeriya hakika ya manta yadda kasar ta ke domin hakan ba zai haifar da komai ba illa rugujewar kasar gaba daya domin babu fahimtar juna da hadin kai da za’a iya yin haka salun-alun. Mu dubi kasar da ba ta da banbance-bance irin namu, wato Libya, amma ta wargaje yayin da ta yi kokarin juyi da karfin tsiya. A lokacin da matasan kuduncin kasar suka fito zanga-zangar matasan na arewa ba wanda ya fito, ina dalili? Shin matasan arewa ba su fi na kudi zama cikin kunci ba? Duk mai hankali zai gane cewa an yi amfani da bangaranci da addini abinda ya sa yan arewa su ka ki shiga, musamman yadda aka rika nuna bidiyoyin Kanu da zantukan inyamurai. Irin wannan dalili shine ya faru a shekarar 2011 yayin da yan arewa su ka fito kone-kone bayan faduwar Buhari amma yan uwansu na kudu ba wanda ya fita. Wallahi mu kiyayi duk ranar da yaran arewa za su yi zanga-zanga tasu ta kansu, domin idan su ka yi ba wanda zai tsira saboda matsin da su ke ciki na rashin ayyuka, shan kwayoyi da kuma fushi da mahukunta.

Ina ganin gwamnati da gangan ta ki kallon hakikar matsalar da matasa ke ciki idan mu ka yi la’akari da jawabin shugaban kasa bayan tarzomar matasa a kudu. Maimakon shugaban kasa ya lallashi matasa ya amsa gazawar gwamnati na kula da halin da su ke ciki sai ya bige da kurin cewa ba wata gwamnati a tarihi da ta fito da hanyoyin tallafawa matasa kamar tasa. Hakika wannan gwamnati ta fito da tsare-tsare na tallafawa matasa fiye da na baya amma magana ta gaskiya a suna su ke kawai domin ba sa kaiwa ga hakikar wadanda aka nufa. Domin bayan jawabin shugaban kasa kadan sai ga matasa a arewa (Kaduna, Jos, Tarab da Adamawa) su na ta balle rumbunan ajiyar kayan abinci suna wawaso. Ya kamata shugaban kasa ya san cewa hakika akwai tsaruka masu ma’ana irinsu na NIRSAL da gwamnatinsa ta samar amma a takarda su ke kawai. Wannan tsari na NIRSAL shi kadai da ya na aiki wallahi sai an ga tasirinsa domin tsari ne wanda zai samar da kudade ga matasa masu kwazo cikin sauki yadda zasu iya kafa sana’o’i da masana’antu, amma akalla kimanin mutane dubu dari shida ake tsammanin sun nema amma idan banda yan tsiraru kuma shafaffu da mai kadai su ka samu. Shi kansa tsarin Ancho borrower ta bayyana karara cewa asara ce ga gwamnati domin akasari ba hakikanin manoma ake baiwa ba shi yasa kudaden basa iya dawowa. Don haka ya kamata gwamnati ta soke shi ta kawo tsarin tallafin noma kai tsaye yadda manoma kadai ke iya cin moriya (samar da iri, filin noma da taki a saukake). Tsarin tallafawa manoma ta hanyar daukar hoton gonakinsu da aka yi a farkon wannan damina ga shi har daminar ta wuce ba abinda aka yi. Kudaden trader-moni sun yi kadan yadda ba za su iya tallafar sana’o’i ba(an ce da ka baiwa mutum kifi gara ka koya masa kamun kifin). Wato duk da yawan tsare-tsare a gaskiya basa aiki kuma abinda zai kawar da matsalar matasa shine a tabbatar da cewa ire-iren wadannan tsaruka dole a yi su a bude yadda duk wani dan kasa da ya cancanta zai iya cin moriyarsu ba sai wadanda ke kusa da yan siyasa ba. Ba wata kasa da za ta kai gaci idan kananan sana’o’inta da masana’antunta basa samun hanyar samar da jari. Gwamnati ya kamata ta tursasa bankuna su rika ba matasan da su ka cancanta basuka ba kawai su rika jibge kudaden da aka sace ba, ba tare juya su ba.

Wasu na ta kokarin kare shugaban kasa da cewa ba laifinsa ba ne laifin wadanda ya baiwa amana ne, duk wanda ya fadi haka ya manta da cewa yan kasa ne su ka ba shi amana kuma ya zabi mutane wadanda ya nuna cewa ya yarda da su dari-bisa-dari domin ba yadda ba a yi ba a baya ya canza shugabannin hukumomin tsaro amma ya yi kemudugus. Don haka ko a gaban Allah idan gwamnati ta yi nasara ko akasarin haka ba wanda za’a dorawa face shi.

Kada mu manta da yan majalisunmu wadanda sun kasance kadangaren bakin tulu domin duk da cewa kasafin kudinsu ya ninka na fadar shugaban kasa kuma ba wanda ya san yadda su ke juya kasafin nasu, amma duk da haka bayan sun lakume nasu kasafin idanuwansu kuma na kan sauran hukumomin gwamnati. Mun ga yadda su ka yi watsi da binciken NDDC lokacin da aka tasarwa tona musu asiri wajen badakalar kwangiloli. Haka nan da yadda su ka kama fada da minister kan ayyuka da za’a ba matasa a kananan hukumomi 774. Daga dukkan alamu mun baiwa kura ajiyar nama ne kawai.

Shawarata ga mahukunta da yan siyasa shine su rage hadama da handama da babakere su karkata wani kaso daga cikin arzikin kasar nan ga matasa, domin wallahi ita ce kadai hanyar da za ta hana yin fito-na-fito da matasan nan ko ba-dade-ko-ba-jima. Duk wata kwaskwarima sabanin hakan sai dai ya jinkirta zuwan wannan rana amma ba ya hana ta zuwa ba. Wannan zanga-zanga da matasan kudu su ka yi kararrawa cewa a gare su, duk ranar da yaran arewa su ka fito irin haka, zai wahala Najeriya ba ta ruguje ba idan mu ka yi la’akari da yadda su ka yi a dalili na siyasa a 2011, ba a dalilin yunwar cikinsu ba. Duk wanda ka kai bango ba shi da zabi illa ya turo ka baya. Allah ya bamu ikon ceton kan mu da kanmu kafin lokaci ya kure.

Comments

Popular posts from this blog

ALAMUN TSINUWA...

LARABAWA: AL’ADA KO ADDINI?

Dabara Ta Rage Wa Mai Shiga Rijiya…