MARTANIN DA NA BA MARIGAYI SHEIKH JAFAR MAHMUD ADAM


Laraba, 29 ga watan  Maris na shekarar 2006, ran ace wadda a ka dade ana dakonta sakamakon yayata zuwan husufin rana da kafafen yada labarai na duniya su ka yi makonni sun a yi. Masana kimiyya sun yi has ashen cewa za’a sami husufi a wannan rana a fadin duniya wanda za’a ga cikakken husufin dag inda zai faro a kasar Brazil ya keto tekun Atalantika, ya bi ta arewacin Afirka ya ratsa tsakiyar Asiya inda zai kare daidai faduwar rana a yammacin Mongolia. Sauran kasashe dab a za su ga cikakken husufin ba sun hadar da kasha biyu cikin uku na kasashen Afirka hard a Najeriya, da wasu kasashen Turai da tsakiyar Asiya. A wannan safiya ina zaune da biro na zan fara rubutun shiri na da na ke gabatarwa na TSOKACI wanda na ke bayanin ayoyin Qur’ani da kimiyya a sabon gidan rediyon Freedom na Kano, sai na jiyo muryar marigayi Sheikh Jafar ya na bayani a gidan rediyon na Freedom inda yake bayani kai tsaye game da wannan husufi ta mahangarsa ta addini. Hakika Jafar na cikin mashahuran malamai das u ka fito daga arewacin Nijeriya saboda iliminsa na larabci da Qur’ani sai dai kawai kasancewar ya na da tsaurin ra’ayi irin na izala. Maimakon ci gaba da rubuta na sai na zauna na saurarin shirin gaba dayansa inda na dauki wasu abubuwa wadanda na ke ganin cewa da kuskure a cikinsu. Sakamakon haka na yanke shawarar mayar masa da martini a cikin shirina na gaba sakamakon ya jibanci abubuwan. Washegari na tafi gidan rediyon Freedom inda na gabatar da shirin.

Da farko dai Sheik Jafar ya zargi turawan yamma da cewa maganar das u ke yi cewa husufi sakamakon wata na shiga tsakanin rana da duniya ne ba daidai ba ne kuma ya sabawa ayar Qur’ani wadda ke cewa

Q36:40 “Rana bay a kamata a gareta, ta riski wata. Kuma dare bay a kamata a gare shi ya zama mai tsere wa yini, kuma dukkansu a cikin wani sarari guda su ke yin iyo”

A fassarar Malam Jafar wannan aya ta kore wancan ikirari na masana kimiyya da ke cewa wata ya shiga tsakanin rana da duniya kuma ya kara da wani hadisin da ke cewa idan ana husufi musulmi su shiga masallatai su yi ta addu’a domin zazzabi yak e. A cikin shiri na, na ambaci cewa dalilin da Jafar da wasu malamai su ka yi wa wannan aya gurguwar fahimta shine sakamakon bas u da ilimin kimiyya, domin da suna da ilimin kimiyya zasu gane cewa hakika wannan aya bat a yi karo da bayanai na kimiyya da lamarin husufi ba ko na Rana ko na Wata. Na ci gaba inda na bada sassaukan misali wanda ko wanda bai je makarantar boko ba zai iya fahimtar hakan. Na yi amfani da misali da agogon bango wanda ked a hannayen dakika, minti da awa wadanda ke cikin farantin agogon. Idan muka dauki farantin agogon inda wadannan hannaye ke zagaye a ciki tamkar shine sararin samaniya wanda Rana, Wata da Duniyarmu ke iyo a ciki. Idan mu ka dauka cewa hannayen dakika da na minti da na awa su ne a maimakon Rana, Wata da Duniyarmu sai mu dauka cewa hannun dakika da ke sama shine rana, hannun minti kuma wata sannan hannun awa kuma duniya. A misalign agogo duk inda sha biyun rana ko ta dare ta yi, wadannan hannaye su kan kasance a layi guda wanda ke tsaye a kan sha biyun, to kamar haka duk sanda rana, wata da duniya a yayin kewayensu su ka tsaya a saitin layi guda shine sanda ake samun husufi. Idan husufin rana ne kaga rana dake hannun dakika idan haskenta ya taho zai tarar da wata da ke tsakiya wanda zai hana hasken nan isa doron duniya maimakon haka sai inuwarsa ta fado kan doron duniya yadda wanda ke duniya idan ya kalli rana sai ya ga duhun wata yak are ta. Haka abin yake a lokacin husufin wata inda duniya ke shiga tsakanin rana da wata yadda hasken rana da dama shi ke haskakka wata sai duniya da ke tsakiya ta kare shi yadda ba zai isa watan ba, a maimakon haka sai mu ga inuwar duniya ta rufe wata yadda zai zama baki babu haskensa.

Don haka duk da cewa wadannan halittu na duniya, wata da rana na iyo a sarari guda ba wanda zai taba wani amma kuma wani na iya kare hasken wani isa wajen wani, abinda ke zama husufi ba tare da karya dokar wani wa baya tarar da wani. Wannan bayani na kimiyya ba inda ya yi karo da waccan aya ta cikin Yasin. Bayani nay a sami karbuwa sosai ga masu sauraro na amma dai dalilin haka ya san a bar ci gaba da gabatar da wannan shiri. Ba anan kawai Malam Jafar ya tsaya ba domin akwai inda yak e cewa idan da duniya na kewaye da sai a ga masallacinsa da ke Gadon a yammacin Kano ya karkata wajajen Tarauni da ke gabashin Kano. Amma shi katantanwa da duniyar mu ke yi abu ne dam asana su ka gano kuma ilimi ne na yakini wanda aka iya tabbatar da sashihancinsa domin shi ne dalilin day a sa a ake sallar Azahar a masallacin Annabi amma sai bayan awa biyu za’a yi azahar din a masallacin Sultan Bello da ke Kaduna. Da duniya bat a katantanwa da lokaci a doron ta zai kasance bai daya a ko’ina cikin duniya amma kasancewar wannan katantanwa shi yasa a ka sami zangogin lokaci goma sha biyu a doron kasa yadda yayin da wani ke shiga safiya wani ke shiga yamma.

Abin day a kamata mu tambayi kanmu shi me yasa manyan malaman ke jahiltar kimiyya wadda yara yan firamare ya cancanta su sani? Shin Qur’ani da Hadisi bas u nuna mana mahimmancin ilimi ba, wanda ya shafi kimiyya da sauran fannoni a matsayin wajibi a san su? Shin neman ilimi bas hi umarnin farko da Allah ya sanarwa da Annabi ba a kogon hira? A littafin Bukhari na farko wato Kitabul Ilm, shin ba akwai hadisai sama da 134 wadanda ke nuna martabar neman ilimi ba?shi ma Imam Gazali ya bude littafinsa na Ihya-al-ulum das ashen ilimi kuma shin ba mu ga yadda Allah ya nuna mana fadin ilimi cikin tafiyar Musa da Kidir na banbancin ilimin annabta da na walittaka ba? Shin ba ilimin kimiyya ba ne ya kai musulmi tsaikonsu a baya yadda su ka kafa daular da ba’a taba ganin irinta ba kafin zuwan musulunci? Musulman bay a su ne su ka gina ginshikin kimiyya wadda duniya ke takama da ita a yanzu amma me yasa malaman mu na zamani da dama ke kyamatar kimiyya, ina dalili? Shin malaman mu na zamani zasu iya yin shura a fannonin ilimi irinsu Ibn Sina, Ibn Rushudi, Ibn Khaldun, Al-Gazali, Al-Haitham da ire-iren magabata wadanda su ka shahara a fanonin kimiyya kama dag a ilimin sararin samaniya, likitanci, falsafa, lissafi da sauransu kuwa?

Amma baa bin mamaki ba ne yadda daga malaman musulmi su ka zama koma baya a fannonin ilimi domin an yi daruruwan shekaru ana cusa abubuwa da sunan addini wadanda ba addinin ba. Musamman idan mu ka dauki yadda Salafiyanci ya bada gudunmuwa ta wannan fanni. Salafiyanci ya fara samo asali daga Imamu Ibn Hanbal (d. 825) daga wancan lokaci su ka yanke shawarar bin hanyar magabata kawai (wato As-Salaf al-salih) wadda Ibn Taimiyya ya inganta (d. 1328) yayin da Muhammad Bn Abdulwahab ya dabbaka. Asalin salafiyanci ya faro da zummar karkade duk wata bid’a da tsayar da sunna, wanda hakan abu ne mai kyau sosai amma kuma wajen aiwatar da hakan sai ya sami matsaloli guda biyu. Matsalar farko it ace wajen yin fassarar Qur’ani kai tsaye yadda ta zo (kamar yadda Jafar yayi wa waccan aya ta Yasain) sannan abu na biyu shine kafirta wanda ya yi sabani da ra’ayi (wato Takfir). Ibn Hanbal shine asalin salafiyanci idan mu ka yi la’akari da komawa kan fassarar kai tsaye ga Qur’ani amma a matsayin darika sai a karni na sha hudu Ibn Taimiyya ya kai ta cikakkiyar darika. Aure tsakanin yunkurin Ibn Abdulwahab da na Ibn Saud a karni na sha takwas ya bada damar amfani da karfin soja wajen kafa daular kasar Saudi Arabia. Mazhabar Hanafi, it ace aka fara kafawa kuma wadda ita kadai ta yarda da amfani da ra’ayin masana wajen kiyas yadda shugabanta ya yi ikirarin cewa “Mu mun yarda da ra’ayi amma ba zamu tilasta wani bin wannan ra’ayi ba idan ka na da hujja wadda ta fi tamu karfi ka zo da ita” da ace duk mazhabobi sun dauki wannan ra’ayi da hakika ilimi ya bunkasa a musulunci musamman a bangaren bincike amma sai mazhabobin Maliki da na Hanbali (wadanda yan salafiya ke bi) su ka kaucewa wannan ra’ayi tare da sukarsa. Shi kuma shafi’I sai ya raba kafa a matsayin mai sassauci tsakianin biyun.

Annabi dai shine annabin karshe kuma musulunci ne saukakken addini na karshe amma duk da haka babu wani mai tafsiri (Mufassir) ko mai ilimin shari’a (Faqih) wanda za’a ce shine mai fassarar karshe ko mai ilimin shari’a na karshe. Amma a farkon karni na goma wadannan mazhabobi musamman karkashin hanbalawa an rufe kofar ijtihadi (bincike na masana) kuma duk wanda ya kaucewa wannan ra’ayi ana ganinsa a matsayin dan bidi’a. Daga wannan lokaci sai kururutar Taqlid (wato karbar hukuncin magabata ba tantama) ya zama rowan dare, duk da cewa dai hakan kuma ba zai rasa nasaba da Mihna (azabtarwa) wadda sarakunan musulunci a lokacin (Mamun, Mu’tasim, Wathiq da shekaru biyu na Mutawakkil) karkashin malaman mutazilawa su ka rika yi wa malamai, musamman yan sunni wadanda ke da’awar cewa Qur’ani ba halittacce ba ne. Imam Hanbali na cikin wadanda aka azabtar tare da daurin kurkuku sakamakon wannan ra’ayi. Watakila wannan lamari na cikin dalilan da yasa ya zama a gaba wajen ganin an rufe kofar ijitihadi. Amma kuma rufe wannan kofa, bayan sabawa umarnin Allah na “Ku tambayi masana, idan ba ku sani ba” na cikin dalilin koma bayan ilimi a musulunci.

Mulkin mallaka da rugujewar daular usmaniyya (Ottomon) ya zaburar da masanan zamani irinsu Sayyid Qutub, Muhammad Abduh da Rashid Rida farfado da ra’ayin rikau a matsayin hanyar das u ke ganin uata za ta ceci al’ummar musulmi daga tasirin turawa, kuma dukkansu sun yi rubuce-rubuce mai yawa a fannin. Kafa madabba’ar Salafiyya da saida littafai mai suna Al-Maktaba al Salafiyya a kasar Misra a shekarar 1909 karkashin jagorancin Muhibb Khatib, ta samar da dimbin littafai ire-iren haka. A lokacin yakin duniya na biyu, A;-Khatib ya sami gayyatar Amirin Makka inda ya je ya kafa madabba’ar Al Amiriyya. Zuwa shekarar 1924 kasar Saudiyya ta kaddamar da buga rubuce-rubucen Imam Hanbali. Cikin littafan farko da wannan madabba’a ta fara bugawa shine littafin Ibn Qayyim wanda Sarki Sa’ud da kansa ya dauki nauyinsa. Wannan ya bude hanyar rubuce-rubuce hanbalawa masu tsaurin ra’ayi kuma nabuga dubban daruruwa wadanda aka rika rabawa mahajjata a kokarin assasa salafiyanci. Zuwa shekarar 1921 an bude wajen saida littafai mai suna Salafiyya a kasar Pakistan da kuma a wani a shekarar 1922 a Damaskus ta Syria baya ga samar da tallafin karatu ga dalibai zuwa jami’aUmmul Qura da ke makka.

An ci gaba da yada Wahabiyanci baya ga rubuce-rubuce littafai da ake baiwa mahajjata kyauta ta hanyar kafa Ribida da wata jami’ar a Madina wadda ita ma ke daukar nauyin dalibai kyauta a horar das u salafiyanci kafin su koma kasarsu su ci gaba da da’awa. A Najeriya kuwa salafiyanci ya samoasali daga yunkurin mutane biyu, wato Ahmadu Bello Sardauna da kuma Sheik Abubakar Gumi bayan sun dawo daga aikin Haji a shekarar 1955. Gumi yayi wa kasar saudiya ayyukan fassara shi kuma Sardauna na cikin iyayen da suka kafa rabida (Muslim World League) a wannan shekara a Saudi. Gumi ya kafa kungiyar Izalatul Bidi’a wadda ta fara da’awa ga mutanen gari yayin da Sardauna ya kafa Jama’atu Nasril Islam wadda ta tunkari yan boko da ma’aikata.

Ta’addanci da muke fama das hi yau a Najeriya kuwa, ko mun ki ko mun so, ba zamu iya raba shi da tsarin Takfir (na kafirtawa) wanda Sheikh Jafar ya assasa a tsawon shekaru sama da goma ya na tafsiri a Maiduguri ba. Tafsirin tsaurin ra’ayi na kiran a yi jihadi da kuma kafirta yan uwa musulmi tare da kyamatar ilimi daga nasara (kamar yadda na bada misalign a sama na Jafar) su ne su ka jawo mana Boko Haram. Jafar mazaunin Kano ne amma Boko Haram bat a faru a Kano ba, menene dalili sai a Maiduguri? Dalili shine can Jafar ya maida hankalinsa wajen wa’azinsa duk shekara kuma mutanen Maiduguri bas u sami wayewar ilimi na addini da na boko ba (idan banda na haddar Qur’ani) sannan talauci da rashin kasuwanci mai karfi ya ja hankali masu ra’ayin rikau irinsu Muhammad Yusuf sun kwankwadi wannan akida ta salafiyanci mai tsauri fiye da malamansu yadda su ka yi watsi da boko kwata-kwata kuma su ke yaki da kimiyya tare da mafani da Takfiranci akan duk wanda bai yadda da ra’ayinsu ba sakamakon day a saka shi kansa Jafar ya kasance mutum babba na farko day an Boko Haram su ka kasha.

Ba a nan Najeriya kawai ba a duk fadin duniya kama daga Afghanistan da Pakistan, zuwa Syria da Bagadaza, a Nigeria, Mali da Somaliya duk kungiyoyin Al’qaeda, Taliban, Isis, Al-Shabab da Boko Haram, sun kasance tamkar  bangaren masu daukar makami ne na kungiyar salafiya kamar yadda kungiyar falasdinawa ked a PLO da Hamas. A yanzu hatta kasar Saudiyya, wadanda su ne suka dauki nauyi da assasa salafiyanci a doron duniya, sun fara dawowa daga rakiyar malamaimasu tsaurin ra’ayi yadda su ka fara cire wasu tsauraran fatawoyi da suka samar a baya domin rage karfin irin wadannan malamai.

Musulunci bai taba samun kansa a tsaka mai wuya irin ta wannan zamani ba saboda yadda turawan yamma su ka sako addinin a gaba sannan a cikin gida ake fuskantar tsatstsauran ra’ayi wanda ya haifar da ta’addanci ga kan mai uwa da wabi. Mafitar musulmi day ace, at yin watsi da duk banbance-banbance na kungiyanci da darika a dunkule waje guda a kwaikwayi hakikar rayuwar da annabi ya yi a Madina. Dole mu gane mahimmancin zabin yin addini yadda Annabi ya nuna a Madina inda ya samar da al’umma dake kunshe da Kiristoci da yahudawa a karkashin adalcin kasa daya. Duniya ta zama dunkulalliya a yau kuma rashin adalci na habaka ta ko’ina, dole mu kalli wancan lokaci na baya mu gane abubuwan das u ka hadamu waje guda amatsayin mutane masu imani maimakon yan izala, yan shi’a ko yan darika domin duk wadannan bajo da muke makalawa juna ba wanda ya sansu lokacin da Annabi ya kafa addinin a madina.

 

 


Comments

Popular posts from this blog

ALAMUN TSINUWA...

LARABAWA: AL’ADA KO ADDINI?

Dabara Ta Rage Wa Mai Shiga Rijiya…