WATA 8 BAYAN KADDAMAR DA TASHAR RUWA TA BARO


Yau kimanin watanni takwas kenan (wato tun January 2019) da shugaba Buhari ya kaddamar da tashar jirgin ruwa ta Baro. Wannan tasha ta samo asali tun lokacin turawan mulkin mallaka da su ka zabi garin Baro ya zama tashar jirgi saboda kasancewar ta a tsawon kilomita 650km tun daga bakin teku a kan kogin Kwara, ba wajen da ke da gabar ruwa mai tsandauri da zata iya jurar shige da fice na jirage da sauke kaya kamar ta Baro ba. Tun a shekarar 1911, lokacin turawa aka hada garin Baro da layin jirgin kasa wanda ya taso daga Kano domin jigilar kayayyaki, musammam amfani gona na auduga da gyada a wancan lokaci. Amma saboda rashin tsari da hangen nesa irin namu ya kasance sannu a hankali sakamakon daina noman gyada da auduga a arewa, sai a ka yi watsi da wannan layi na dogo, kuma ita ma tashar ta mace murus.

Wannan tasha ta Baro ta na da alaka da shugaba Buhari kasancewar a lokacin da ya ke rike da hukumar PTF su ne suka tsara yadda za’a sake gina wannan tasha ta zama ta zamani. Gwamnatoci a baya, musamman ta Abacha da Yar’Adua sun yi yinkurin yashe kogin kwara tun daga Warri zuwa Baro domin samun damar jiragen daukar kaya su rika isowa har Baro. Yunkurin bai kai ga nasara ba har lokacin Jonathan wanda ya ware Naira Biliyan 47 kuma a ka sakar wa ‘yan kwangila hudu kimanin Biliyan 34 domin aiwatar da wannan aiki. A karshe dai an wayi gari babu kudin kuma ba’a yi aikin ba. Gwamanatin Buhari ta farfado da maganar yashe kogin da kuma gina wannan tasha, inda ministan Sufuri, Amaechi, ya rika cika bakin cewa gwamnatin Jonathan ta wawashe Naira Biliyan 47 kuma ba’a ga komai a kasa ba don haka su za su yi amfani da hukumar da ke kula da hanyoyin ruwa ta kasa (NIWA) wajen yashe kogin a kan Naira Miliyan Dari kacal. Wani bincike da jaridar Daily Trust ta yi game da wannan aiki ya nuna cewa har yanzu dai ba ta sake zani ba game da yashe kogin Kwara domin dai a fadar wani injiniya na ruwa Abdullahi Makujeri cewa ya yi “A ka’ida ana bukatar zurfin da ya kai mita 8.5 zuwa 10.5 yadda manyan jirage za su iya bi yadda za su lodawa kananan jiragen kaya domin isa gaba” to amma a yau zurfin tashar Baro bai karasa mafi karanci na mita 2.5 da ake bukata ba. Don haka duk wanda ya ce a yau manayan jirage za su iya isa tashar Baro ya na yin yaudara ce irin ta siyasa. Shekaru takwas ke nan da ake cewa an yi yasar wajen, wadda a ka’ida ko da an yi, ana bukatar bibiyar yasar duk bayan shekaru biyu wanda ba’a taba yi ba.

Wani muhimmin al’amari game da aikin wannan tasha shine na maganar wutar lantarki, domin babu yadda za’a yi a gudanar da al’amura na wannan tasha idan muka yi la’akari da manyan injuna na dagawa da daukar kaya da ma’aikata da ofisoshi da ake bukata idan babu wutar lantarki. Abin mamaki shine har yanzu garin Baro ba’a hada shi da layin wuta na kasa ba. Tasha ce wadda za ta kunshi kusan ilahirin bangarorin ma’aikata na tsaro, yan sanda, sojoji, hukumar shige da fice da ta baki da sauransu domin tasha ce tamkar filin jirgin sama ko ta jirgin ruwa. Idan ba wutar lantarki ta yaya aiki zai iya wanzuwa a wannan tasha?

A daya hannun kuma, ita kan ta tashar ta Baro, gwamnatin Jonathan ta bada kwangilar gina ta a kan Naira Biliyan 5.8 a shekarar 2012, abinda shi ma ya zama labari. Zuwan Buhari ya farfado da maganar kwangilar gina tashar kuma an kama aiki domin ganin an samar da gabar tasha mai tsawon mita 150 da kuma wajen sauke kaya mai fadin murabbain mita 7000 da kuma wajen tsayawar jirage mai fadin murabba’in mita 3,600. A farkon watan Janairu na wannan shekara shugaba Buhari da ‘yan tawagarsa sun sauka a garin Baro a jiragen Helikwafta domin kaddamar da wannan tasha, sakamakon cewa babu wata hanyar mota ko jirgin kasa ingantacciya da za su iya bi domin isa garin Baro. Hanya mai tsawon kilomita 55 da ta ratsa garuruwan Baro-Katcha-Agaie da kuma ta Baro-Muye wadda ke haduwa da garin Gegu da ke kan babbar hanyar Abuja-Lokoja, dukkansu ba za su iya biyuwa ba. Ita hanyar Baro-Katcha-Agaie gwamantin Yar’Adua a kokarinta na farfado da wannan tasha ta bada aikin gina wannan hanya tun a shekarar 2009 amma daga baya a shekarar 2012 sai Gwamnatin Jonathan ta soke kwangilar bisa hujjar cewa dan kwangilar ya kasa yin aikin yadda ya kamata. Amma daf da zaben 2015, sai gwamnatin ta Jonathan ta sake bada kwangilar wannan titi ga wani kamfanin India a kan kudi Naira Biliyan 17.5 da yarjejinar za’a kammala aikin a watanni sha biyu. Da Buhari ya ci zabe, an saki wani kaso na kudin aikin wannan hanya amma sakamakon kasa ci gaba da bayar da kudaden aikin wannan hanya, har yanzu bai fi kilomita goma ba cikin abinda aka kammala, dalilin da ya sa tawagar shugaba Buhari ta sama su ka iya isa Baro a watan Janairu lokacin kaddamar da tashar. Sassa na wannan hanya, musamman tsakanin Katcha da Baro a lokacin damina ba ya biyuwa sakamakon cabi da kwazazzabai, sannan su kansu gadojin da ke wannan hanya sun fara gazawa domin wasu tun na zamanin turawa ne. Haka abin ya ke a sashen hanyar Baro-Muye-Gegu wadda ke hada garin Baro da sashen kudancin kasar nan.

Wani tsohon soja wanda jaridar Daily Trust ta yi hira da shi ya ce “Tsawon watanni takwas da kaddamar da wannan tasha babu wani jirgi ko da guda da ya iso tashar Baro” inda ya ci gaba da cewa “Ta yaya jirgi zai zo tunda babu kayan aiki a wurin wanda zai bada damar hakan?” A tashar kawo yanzu babu wasu jami’an shige da fice da ke wajen. Wani mai gadi ya ce kafin zuwan shugaban kasa an je an yi fentin katangar wajen an saka wayoyi masu tsini na tsaro a kai. Shi kan sa kamfanin First Index Nigeria Limited wanda aka bawa kwangilar kula da manyan kugiyoyi na daukan kaya sai da ya koka a karshen shekarar 2018 saboda motar da ta dauko kayan da ake gaggawar su isa garin Baro kafin zuwan shugaban kasa, ta kafe a kan hanya kafin ta isa, sai da hukumar kula da hanyoyin ruwa NIWA ta sa aka je a ka yi aikin hanya kafin a samu wannan mota ta isa Baro da karafunan da aka nuna wa duniya kamar tashar ta kankama.

A bayyane ya ke cewa wannan gwamnati, ta yi amfani da wannan aikin na Baro domin kamfe na siyasa kamar yadda sauran gwamnatoci a baya su ke yi. Kuma abin tambaya anan shine idan wannan gwamnati tsawon shekaru biyar ba ta iya kamala wannan aiki ba, kuma bayan watanni takwas da kaddamar da tashar da aka yi na yaudara, ba tare da an ci gaba da maganar hada garin Baro da wutar lantarki ba, ko gyara hanyoyi biyu da su ka hada arewaci da kudancin kasar nan da tashar ba, sannan shi ma hanyar jirgin kasan ba’a kammala shi ba ballantana yashe kogin daga matsayinsa na kasa da mita 2.5 a yanzu ya kai akalla mita 8.5, shin duk wadannan za su iya samuwa a sauran shekaru uku da su ka rage wa wannan gwamnatin?

Comments

Popular posts from this blog

ALAMUN TSINUWA...

LARABAWA: AL’ADA KO ADDINI?

Dabara Ta Rage Wa Mai Shiga Rijiya…